MATSATSUBI LITTAFI NA UKU PART I NA: ABDUL'AZIZ SANI MADAKIN GINI


 

MATSATSUBI LITTAFI NA UKU PART I 
NA: ABDUL'AZIZ SANI MADAKIN GINI 


🤴

POSTING: NAJIBULLAH MUHAMMAD ☝️☝️

TYPING: HABIBULLAH MUHD KABARA ✍️✍️


https://www.facebook.com/groups/332169966389024/?ref=share


MARUBUCIN YACI GABA DA CEWA....


Yɑku abokan tafiyata ina mai sanar daku cewa gwagwarmayar da muka sha abaya tamkar sharar fage ce akan wacce zamu tunkara agabanmu

ina mai rokonmu damu kara  damu kara zage dantse

mucire tsoro da fargabar komai domin matsoraci baya zama gwani

ko wanene ko dan wa

musa aranmu cewa ko mu mutu ko muyi rai 

sai mun kai gaci, ku tuna cewa akwai sauran

aiki agabanmu don haka zamanmu anan tamkar hutun jaki da kaya aka ne

ina mai umartarmu damu tashi mu kara gaba

ba zamu tsaya ako'ina ba harsai mun karar da dukkannin dodannin dake cikin wannan daji

koda sammaru ya zo nan azancensa saiya zare takobinsa ya dagata sama

yayi kururuwa

irin wacce ke firgita maza afilin daga

nantake kururuwar tasa 

ta cika dajin harda amsa kuwwa izuwa nesa

al'amarin daya janyo hankalin sauran  kabilun dodannin 

kenan suka san cewa lallai yau sunada baki

don haka sai kwadayi ya kamasu, suka fara tande baki

suna dalalar da yawu akasa, 

lokacinda yarima sammaru suka gama rurinsu

don karawa kansu kaimi da kuzari sai suka dane bayansu guluz 

sukaci gaba da tafiya a sama cikin tsananin gudu

aikuwa cikin kankanin lokaci suka riski kabilar dodanni ta uku

ana haduwa yaki ya barke akayi dauki ba dadi 

wohohoho

awannan rana rayuka sun salwanta, jini kuwa ya malala

don saida ya zamana koramai da fadamomin dajin

sun rine sun zama jini maimakon ruwa

awannan gumurzun da akayi ne da kabilar dodannin ta uku yarima lubaiku ya rasa rayuwarsa 

domin saida dodannin sukayì walima da sassan jikinsa

ba'a samu komai ba daga barin jikinsa hatta gashin kansa 

saida suka cinye tabbas awannan lokaci su yarima sammaru 

sunga tashin hankali irin wanda basu taba ganiba

alokcinne aka cirewa boka karluz kunnuwansa aka cinye 

shikuwa yarima larbuz saida ya rasa 'yan yatsun hannunsa na hugu

babu wanda ya bada mamaki kamar yarima lauhana domin

duk da kasancewar kafarsa daya zamewa dodannin alakakai

yayi musu muguwar barna domin saidaya kashe sama da guda dubu uku shi kadai

kuma har aka gama yakin saidaya sami rauni ajikinsa

inbanda sammaru da ashwarya babu wanda bai samu mugun rauni ba a wannan yakin

bayan an gama yakin ne su duka suka zauna suka fashe da kuka

bisa tunawa da irin mutuwar da yarima lubaiku yayi

gaba dayansu sai jikinsu yayi sanyi hankalinsu ya dugunzuma 

kowa zuciyar sa ta fitar da rai ga rayuwa

kuma sukayì nadamar baro kasashensu da sukayì 

don cika wannan buri nasu mai matukar hadari

anan ne dare ya riskesu kuma yunwa d kishirwa 

ta addabesu bisa dole aka kunna wuta aka zagayeta anajin dumi

saboda hunturun sanyin dake kadawa sannan aka fara

tunanin yadda za'a samu abinci da ruwan sha 

tunda shi kansa ruwan dake dajin ya zama jini 

anacikin yin shawarane boka karluz ya dubi aljani guluz yace

kune aljanu ina dabara? ko zakuje kudan zagaya

ku samo mana abinci da abinsha? 

guluz yace haba bakaji kunyaba ka fadi haka

ka tuna cewa kai bokane zaka iyayin tsafi  abinci da abinsha su bayyana nantake 

karluz ya daka masa harara yace

baka da hankali, ai kasanma idan na mayi tsafin wani aljaninne zai kawo

kasan kuwa babu wani aljani dazai iya shigowa

cikin jejin nan don ya tabbatar da cewa halaka zaiyi

ai kawai ku cire tsoron komai kuje ku samo mana abinci 

abinci dai idan kukayi hakuri mun kusa rabuwa daku 

tunda saura jeji biyu kacal mu iso takiyar duniyar nan 

cciki damuwa da tsoro boka guluz yace 

shikenan 

munyarda zamuje mu nemo muku abinci amma ka duba

mana cikin madubin tsafinka inda zamuje mu nemo muku abinci 

batareda munsha wahalaba ko mu afka cikin bala'i

boka karluz ya bushe da dariya yace 

oh! waiyau aljani ne da tsoro kamar farar kura

nandanan ya fiddo madubin tsafinsa ya ajiye a kasa 

ya shafeshi

saiga hoton wata katuwar barewa kwance acikin wani rami

acan gaba kadan daga inda suke zaune yanzu 

kuma abayan ramin wata korama ruwa na gudu 

acikinta mai kyau da haske wanda jini bai gurbatashiba

agaba daya harabar wajen babu alamar dodanni 

koda ganin haka sai aljani guluz ya dubi aljani amzil 

da hurus yace maza kuje ku dauko barewarnan

kuma ku debo ruwan koramar nan isasshe 

ku kawo musu, kafin ya gama rufe bakinsa 

tuni su amzil sun bace, saida dakika dari uku da sittin ta wuce 

amma basu dawoba, al'amarin daya tayarda hankalin kowa kenan

gimbiya ashwarya tace 

kai jama'a ruwafa baya tsami banza

lallai akwai abindaya faru ga su amzil donya kamata ace sun dawo

tun dazu, kodajin haka sai boka karluz yace 

kwarai kuwa hakane kinyi gaskiya

amma bara mu duba muga halinda akeciki

cikin sauri ya sake fiddo madubin tsafinsa ya ajiye akasa ya shafe shi

saiga hoton aljani amzil shikadai 

asama daukeda barewa da kumA ruwa

acikin babbar batta

duk jikinsa jina jina yana tafe yana kayi asaman kamar zai fado kasa

koda ganin haka sai Hankalin su ta sake dugunzuma 

ba'a jimaba saiga aljani amzil ya fado agabansu 

yana kakarin mutuwa nanfa kowa ya manta da batun yunwa da kishirwa 

akazo kan amzil aka tsaya

aljani guluz ya tallafo kan amzil ya dora akan cinyarsa

yana mai kallon fuskarsa yace

yakai dan uwana mai ya faru gareku kaida hurus na ganka cikin wannan hali

cciki matukar karfin hali amzil yace

yakai guluz kayi sani cewa alokacinda

muka shiga cikin kogon nan

don kama barewarnan bamu fuskanci matsalar komai ba

har muka fyadeta ta mutu sai bayan mun fito daga cikin kogon 

sai kawai mukaga wasu irin dodanni sunyi mana kawanya

kafin mu yunkura sunfara kai mana cafka

mukuwa saimuka fara kokarin ceton kanmu

inaji ina gani suka kama hurus suka dinga yaga jikinsa 

sunaci saida suka cinyeshi tas, nikuwa dama iyakar karfina nake yakarsu

dayake su biyarne kacal saina zame musu alakakai 

kasancewar nafisu karfi saida suka kusan hallakani

dakyar ma samu na tsere musu, koda yake tsiran banza nayi don na tabbatar mutuwa zanyi 

yakai guluz ina mai rokonka daka kula da matata

idan har kana da sauran kwana aduniya kuma ka sami damar komawa gida 

kasani cewa matata tana da tsohon ciki

haihuwa yau ko gobe

idan ta haihu lafiya kuma ta sami da namiji kasa masa sunana

idan kuwa macece asamata suna muddarul ikisina 

don ta zamo abin tunawa da iyakar rayuwata

koda amzil yazo nan azancensa  sai idanunsa 

suka kafe, komai na jikinsa ya daina motsi

guluz ya rungume gawar amzil ya fashe da kuka

al'amarin daya karya zuciyar sauran aljanun kenan

wato karmash, karfil, da azgar suma suka kama kuka

saida aka dan jima ana alhilin wannan mutuwa ta aljani amzil 

sannan aka gasa naman barewar nan kowa yaci ya koshi 

akasha ruwa, daga nan sai yarima sammaru ya tashi

ya koma gefe daya ya zauna yana mai tunanin gida 

koda ya tuno da mahaifinsa sarki alyasil buhus

ya tuno halin daya baroshi na kamuwa da cutar mutuwar rabin jiki

saiya fashe da kuka, sammaru ya sake tuno lokacinda mahaifiyarsa

ta rungumeshi tana kuka

sa'adda da  suke bankwanan rabuwa

kawai saiya rushe da kuka

al'amarin daya jefa gimbiya ashwarya cikin tausayi kenan

ta taho ga sammaru da zuwa ta zauna dafdashi

ba tareda ta kalli fuskarsa ba tace

yakai abokina kayi sani cewa 

aduniya babu abindaya fi dadi sama da zama da masoyi

tabbas nasan kana tunanin iyayenka ne

'yan uwanka, danginka da kasarsu

shine sanadin wannan kuka naka

kayi sani cewa nima na kasance acikin irin wannan tunani naka

kuma duk da kasancewata 'ya mace ban bari

kukana ya fito filiba

amma nayi na zuci harnagaji, inason mu kasance masu hakuri 

domin ya zama wajibi agaremu

koda ashwarya tazo nan azancenta sai yarima sammaru ya dago kai

ya dubeta inda yaga kwallah cike a idanunta 

nan take yaji tausayi da kaunarta sun dabaibaye zuciyarsa

baisan sa'adda ya saki murmushiba agareta

jim kadan sukayi shiru su biyu dayansu bai ce uffan ba

daga can sai sammaru ya katse shirun 

da cewa

yake kawata hakika tun lokacinda na baro gida naji ina cikin kadaici

fargaba da rashin kwanciyar hankali 

amma kuma sanda na farajin kalamanki sai naji duk wadannan abubuwa sunyi kaura daga gareni

aduk sa'adda na kalleki ko naji muryarki

sainaji kamar ina cikin gidanmu ne

tareda iyayena da 'yan uwana

tabbas duk wanda ya sami mace kamarki mai dadadan kalamai

masu tausasa zuciya ya gama morewa don ko abakin

kura yake bazaiyi fargaba da bakin ciki ba

koda yarima sammaru yazonan azancensa sai ashwarya taji wani irin farinciki ya baibayeta

take itama taji ta kamu da tsananin kaunarsa

batasan sa'adda ta kura masa ido ba

harsuka shagala da kallon juna

duk wannan abu dake faruwa larbuz, yauhana, da karluz nadaga can gefe suna kallo.

https://www.facebook.com/groups/332169966389024/?ref=share


MU HADU A PART J DON JIN CIGABAN WANNAN KAYATACCE KUMA KASAITACCEN LABARI ✍️

Najibullahi Muhammad 

#LEGENDs.

Next Post Previous Post
No Comment
Add Comment
comment url


';