MATSATSUBI LITTAFI NA UKU PART H
MATSATSUBI LITTAFI NA UKU PART H
**MATSATSUBI**💥💥
LITTAFI NA UKU ✍️✍️
PART H ❤️❤️Hbad:";xgn
NA: ABDUL'AZIZ SANI MADAKIN GINI 🤴
POSTING: NAJIBULLAH MUHAMMAD ☝️☝️
TYPING: HABIBULLAH MUHD KABARA ✍️✍️
GORON JUMA'A ❤️🙏
https://www.facebook.com/groups/332169966389024/?ref=share
MARUBUCIN YACI GABA DA CEWA.....
Guluz yayi dariya yace
aikoda maganin ya kare nasan 'yan uwana
bazasu tafi su barni ba
kasan muna da matukar hadin kai
da dai su tafi su barni gwara su tsaya duk
abinda
zai sameni ya samesu gaba daya
kodajin haka sai gimbiya ashwarya ta tsoma
baki acikin zancen tace
au kana nufin ku aljanu bakwa tsoron mutuwa
nikam ina ganin idan sukaga wani bala'ìn zasu
iya guduwa su barka
guluz ya sake bushewa da dariya yace
aimu aljanu muna da son junanmu
fiye da mutane
kuma munsan mahimmancin alkawari bama
karya shi
ku kuwa mutane akan dukiya ma kuna iya karya
alkawari ko kuci amana
wannan batu ba karamin haushi ya baiwa
gimbiya ashwarya ba
ta bude baki zata mai d raddi sai yarima
sammaru
ya tari numfashinta da cewa
hirar nan ta isa haka kuzo muci gaba da tafiya
cikin hanzari ya haye bayan aljani guluz ya zauna
koda ganin haka sai dukkansu suka hau kan
sauran aljanun
alokaci guda aljanun shida suka tashi sama
tafiyar rabin sa'a sukayì kacal suka iso nahiyar
wadansu manyan dodanni wadanda suka
kasance dogaye zankala zankala
saboda tsawon su duk sun kere bishiyoyin dajin
da tsaunika
koda wadannan dodannin suka hango su
yarima sammaru
asama 'yan kanana kamaI'm tsuntsaye zasu
gifta
ta samansu sai suka daga kawunansu sama
suka wangame bakunansu suka hura musu
wata iska mai tsananin karfi wacce inda acikin
garice zata iya rushe gidaje.
kuma zata iya daukar mutane ta rinka yawo
dasu asama
nan da nan gagarumar iskar ta birkita hankalin
su yarima sammaru da
aljanun shida ya zamana sun kasa gaba sun
kasa baya
kuma sai gware suke da juna, tabbas idan aka
kara 'yan dakiku ahaka
zasu iya hallaka, cikin karaji yarima sammaru ya
baiwa su guluz umarnin saukowa kasa
nantake kuwa suka bi umarnin
kafin su iso kan turba tuni jaruman shida sun
zare takubbansu
suna dira kasa wuri ya hautsine da rurin mazaje
dana dodannin
wannan karon sai su yarima sammaru suka
gane ruwa ba sa'an kwando bane
domin saran dodannin suke amma
kamar a banza domin dodannin sun kasance
masu tsananin juriya
karfi da taurin kai
nanfa dodannin suka kuntata musu yazamana
su
yarima sammaru basa iya komai sai kokarin kare
kai
ana cikin hakane wani dodo ya kama kafar
yarima yauhana ya
karyata da karfin tsiya
yauhana ya kwarara uban ihu cikin dimaucewa
kafin yauhana yayi wani yunkuri tuni dodon
ya saka kafar gaba daya abakinsa ya gutsireta
da bakinsa
ya kama ci kamar mutum yana asuwaki da
cinyar kaza
nantake yauhana ya sulale kasa sumamme
koda ganin abindaya faru sai yarima sammaru
ya
fusata ya daka tsalle sama tun a saman yarima
sammaru ya
zare wata rantsatstsiyar wuka kawai saiya duro
akan dodonnan dake cin kafar yauhan
take ya luma masa rantsatstsiyar wukar a
tsakiyar kansa
kuma ya zareta da karfin tsiya take jini ya kama
tsartuwa asama kamar an fasa goran ruwa
nanfa dodon ya kama make make da ruri ya fadi
nan
ya tashi can har rai yayi halinsa
wannan ce damar da jaruman shida suka samu
suka gano makasar dodannin
don haka suka ci gaba da saransu da sukarsu
aka
kawai sai gani akayi dodannin suna zubewa
kasa matattu
a wannan lokacin ne yarima sammaru ya samu
dama y kwararawa yarima lauhana
wannan ruwan maganin
a karshen cinyar guntulalliya
take wajen ya bushe kamar anfi shekara da
gutsure kafar
adaidai wannan lokacin ne wasu dodanni suka
kawowa yauhana sura don su karasa cinyeshi
cikin zafin nama sammaru ya daukeshi ya
azashi abayansa
sannan ya kaiwa dodannin sara aka alokaci
guda
cikin sa'a kuwa ya raba musu kawuna Kamar an
datsa kabewa
gida biyu take suka zube kasa matattu
nanfa aka cigaba da ragargazar dodannin nan
saida aka shafe sa'a uku
ana gumurzu sannan aka karar da dodannin
awannan yaki babu wanda bai samu rauni ajikin
sa ba
sama da guda uku
yarima sammaru ne kadai ya sami rauni biyu
daya akafarsa wani dodo ya yankeshi da farcen
hannu
daya kuwa a cinyarsa aka caka masa kahon ka
wanda saidaya durkusa kasa yana mai ihu
amma cikin tsananin juriya ya sake mikewa
tsaye
yaci gaba da sara da suka her aka gama yakin
yarima lauhana
yana sabe akafadar yarima sammaru kuma
asume
gimbiya ashwarya ce kadai tayi jarumtaka
kwatankwacin irin wacce
yarima sammaru yayi, amma itama ta sami rauni
abayan kafarta
saikuma larbuz wanda ya taka mahimmiyar rawa
awannan yaki
gaba dayan su dai babu wanda baisha wahala
da samun raunika da yawaba, don har jirine ya
rinka dibarsu saida
sammaru ya kai masa daukin magani
da gaggawa sannan ya dawo hayyacinsa
bayan an gama yakinne kowa ya sharbe akasa
harda suma aljanun shida
sai yarima sammaru ya bisu daya bayan daya ya
saka
musu magani aci wukansu
saidaya gama da kowa sannan yaje kan gimbiya
ashwarya wacce
take zaune agefe guda akan wani karamin dutse
koda yazo gareta ya kalleta sama da kasa baiga
wani rauniba
saiya juya da nufin tafiya
ya zaka tafi baka samini magani ba?
ta tambaya tana murmushi
cikin mamaki yarima sammaru ya waigo ya
dubeta yace
ai banga rauni ko daya ba ajikinki
ashwarya tace baka duba sosai bane
zagayo bayana ka kwaye rigata ka ga ʀɑuɳi
batareda d gardama ba yarima sammaru ya sa
hannunsa zai kwaye rigarta sai hannunsa
ya kama kakkarwa, bakomai ne ya haddasa
hakanba
face ganin kyakkyawan surar jikinta da kuma
fatarta
mai tsananin haske da laushi, duk da cewar
raunin dake bayan nata na da dan girma
amma bai razana sammaru ba kamar yadda
kyakkyawan jikinta
ya razanashi, kamar tasan halin daya shiga sai
tace
me kake jirane ko kuwa kaima zuciyar ragwaye
gareka ciwon y firgita ka
sammaru yayi murmushi yace
ai abin tsoro baya firgita mazajen kwarai
saidai abin mamaki
hakadai ya daure ya zuba mata maganin
hannunsa na karkarwa
bayan ya gama da ita saiya juya don ta koma
inda yake
ba zato ba tsammani saiyaji ankira sunansa
cikin mamaki ya waigo suka dubi juna tana mai
murmushi agareshi
zauna nan abinda tace dashi kenan kawai
sammaru ya zauna
yana mai mamakin hakan kawai saita karbi
kuttun maganin
dake hannunsa ta fara zubawa akan rauninsa
dake cinya
gaba daya. jaruman nan kuwa da aljanun nan
shida sai suka zuba musu ido
tuni awannan lokaci kishi ya turnuke yarima
lubaiku da larbuz
idan na barka kasa maganin da kanka
banyi maka adalciba
domin kai kadai kasawa kowa maganin nan
kamata yayi kaima ayi maka kara
koda jin wannan batu sai sammaru ya yi
murmushi yace
nagode ammafa inason zama da mutumin dake
da kara
kuma inason zama da mace mai zuciyar maza
ashwarya ta bushe da dariya sannan tace
daina kodani haka karkasa
kaina y fashe in banda abinka ina abin yake
ai gadai mAce can mai zuciyar maza tana
kafsawa dasu
cikin mamaki sammaru yace
wakenan kike nufi?
gimbiya fauwaz mana
duk lokacinda na tunoda lokacinda boka
hulumul bakahur
ya nuna mana ita amadubin tsafinsa sa'adda
take ragargazar maza
sai naji kishi ya kamani tabbas fauwaza ta fini
jarumtaka
da kyau nesa ba kusaba
ace nice ita da dolene na shahara ko ina acikin
duniya
awannan zamani, sammaru yayi murmushi yace
ai yanzu ma zaki shahara aduniya idan her kika
sami nasarar
shiga cciki kogon muddarul ikisina kika debo
ruwan
tsumin tsafin bokanya tazubul luhucul acan
taskar tsafinta
kodajin haka sai ashwarya tayi ajiyar zuciya tace
tana zaton dayanmu zai iya cika wannan buri
ka sani cewa naji daga bakin manyan bokayen
duniya cewa
fiye da shekaru dubu baya
babu wani mahaluki daya taba shiga cikinsa ya
fito araye
don haka ba shigar bace wahalaba fitowarce
wahala
sammaru ya jinjina kai yace
hakika zancenki dutsene, to amma ai ance
faduwar gaba asarar namijine
dadai mu zauna mu zuba ido muna gani
iyayenmu su hallaka
gwara muma mu hallaka kan kokarin cetonsu
kafin ashwarya tace wani abu saiga boka karluz
ya taho garesu
da zuwa ya durkusa agabansu sannan ya fiddo
madubinsa na tsafi ya ajiye agabansu
yace, yakai sammaru jagoran tafiya kayi sani
cewa
zan iya nuna maka sauran hadarin dake
gabanmu acikin dajin nan yanzu anan wurin
cikin murna sammaru yace
maza ka nuna mini don musan matakin da zamu
dauka
nantake karluz ya shafi madubin tsafinsa
saiga hoton wadansu dodannin acan gaba
wadanda sunfi n baya girma daban tsoro
madubin ya sake nuna wasu acan gaba suma
sunfi na baya harsaida madubin ya nuna
kabilar dodanni kala biyar wato idan aka hada
dana baya
sunzama kabila bakwai cif cif koda gama ganin
su
sai hankalin sammaru dana ashwarya ya
dugunzuma
nan take sammaru yakira su lubaiku suma suka
gani
awannan lokaci ne yarima yauhana ya farka
daga dogon suman
da yayi
koda yaga kafarsa ta hagu a guntule saiya rusa
ihu
ya fashe da kuka, da kyar sammaru ya
rarrasheshi
ya daina kukan bayan nan sai sammaru ya dubi
jaruman duka
daya bayan daya yace.
https://www.facebook.com/groups/332169966389024/?ref=share
MU HADU A PART i DOMIN JIN CIGABAN WANNAN KAYATACCE KUMA KASAITACCEN LABARI ✍️