An ƙaddamar da rundunar tsaron ƴan-sa-kai ta Zamfara

 



An ƙaddamar da rundunar tsaron ƴan-sa-kai ta Zamfara


Gwamnatin jihar Zamfara ta kaddamar da wata rundunar `yan sa-kai don yaki da `yan bindiga da saura miyagun laifuka a jihar, wadda aka yi wa lakabi da `Askarawan Zamfara`.

Jihar Zamfara dai na cikin jihohin da matsalar `yan bindiga masu satar mutane don karbar kudin fansa ta yi kamari a shiyyar arewa maso yammacin Najeriya.

Rundunar mai suna Askarawan Zamfara ta kunshi zarata 2,646, wadanda aka harhada daga kananan hukumomin jihar 14, wadanda suka samu horo na musamman daga jami`na tsaro da kwararru daban-daban a fannin tsaro don tunkarar matsalar `yan bindiga masu satar mutane da dabbobi a jihar Zamfara.

Da yake kaddamar da rundunar yau a Gusau, babban birnin jihar, Gwamna Dauda Lawal ya ce gwamnatin jihar na amfani da hanyoyi da dabaru daban-daban wajen yaki da miyagun laifuka a jihar, ciki har da kafa rundunar Asakarawan da nufin inganta tsaro a jihar Zamfara, wadda ya ce da yaddar Allah kwalliya za ta biya kudin sabulu.

Next Post Previous Post
No Comment
Add Comment
comment url


';